31/08/2025
Wani Miji ya tambayi matarsa:
“Me mutum yake rasawa idan ya yi aure, kuma me yake samu?”
Matar ta yi murmushi da hikima ta ce:
“Namiji yana rasa zaman kansa na samartaka, ’yancin yanke ƙananan hukunci shi kaɗai, da kuma damar yin abubuwa ba tare da yin la’akari da nauyin da ya rataya a kansa ba. Amma a gefe guda kuma, yana samun abokiyar rayuwa, uwa ga ’ya’yansa, gida da ke cike da dumi da annashuwa.”
Sai mijin ya yi dariya ya ce: “To fa game da farin ciki fa?”
Ta amsa tana murmushi: “Farin ciki, ya kai masoyina, mu ne kanmu ke gina shi. Idan muka ɗauki aure a matsayin rabon ɗaukar nauyi tare da raba farin ciki da nasara, to za mu kasance da farin ciki. Amma idan muka gan shi a matsayin asara, to kullum za mu kasance cikin rashin gamsuwa da asara.”
Mijin ya yi tunani a kan maganarta, sannan ya tambaya:
“Kin fi sona ko kuwa kina son ’ya’yanki fiye da ni?”
Ta amsa ba tare da jinkiri ba:
“’Ya’yana.”
Sai mijin ya yi mamaki ya ce: “Me ya sa?”
Ta ce: “Saboda su jinin jikina ne, ruhina ne.”
Ya ce yana murmushi: “Ni fa?”
Ta yi dariya ta ce: “Kai abokin tafiya ne a wannan hanya, wani lokaci kana faranta min rai, wani lokaci kuma kana bakanta min!”
Bayan wannan tattaunawar, mijin ya zauna yana tunani: Shin da gaske ne alaƙar ma’aurata tana ginuwa ne akan sadaukarwa? Kuma shin waɗannan sadaukarwar ana darajasu da gaske?
A cikin al’ummarmu, ana ganin mace ce ginshiƙin gida. Ita ce uwa da take yin daren tsakar dare tana kula, tana dafa abinci, tana koyarwa, tana tarbiyya, tana tsabtace gida, tana jinya, tana tallafa wa kowa cikin gida. Ita ce take ɗaukar dukkan nauyin rayuwa cikin shiru amma tana murmushi a fuska duk da gajiyarta.
Idan yaro ya yi rauni a makaranta, sai a ce: “Ina mahaifiyar tasa?”
Idan yaro bai da hali mai kyau, sai a ce: “Uwa ba ta tarbiyyantar da shi ba!”
Idan miji bai da farin ciki, sai a ce: “Matar ba ta yi iya kokarinta ba!”
Idan gida ba shi da tsafta, sai a ce: “Uwa ba ta yin aikinta kazamiya ce!”
Amma gaskiyar magana, mace tana yin aiki babba kwarai. Ita ce makaranta a zahiri, amma har ma fiye da haka. Ita ce likita da ke warkar da rauni, malama da ke dasa kyawawan dabi’u, mai ba da shawara, jinya mai kula da ƙanana da manya. Ita ce ɗakin karatu da ke ɗauke da hikimar rayuwa, ita ce zuciyar da ke bugawa da sadaukarwa, ita ce kashin bayan gida da al'umma.
Saboda haka, gaisuwa daga zuciya ga kowace mace da ke ɗaukar nauyin rayuwa babba da ƙanana, wadda take sadaukar da jin daɗinta da farin cikinta saboda wasu, wadda ke kawo farin ciki ga kowa duk da ƙalubalen datake fuskanta.
Ya ke mace, ki yi murmushi ki kuma yi alfahari da kanki, domin ke ce mai haifar da al’umma, tushen ƙarfi da ƙauna a duniya, Kamal yana muku jinjina