02/06/2026
Tunda suna na ya fito, ba yadda na iya dole sai na ce wani abu duk da dai ba zai yiwu a fadi komai ba.
Mu uku ne mu ka zauna mu ka rubuta Bill sakamakon abunda gwamnan jahar Imo na lokacin, Rochas Okorocha, ya shigo da shi na yiwa mutanen Arewa rijista da kuma basu ID card da za su rika yawo da shi. Bill din kwata-kwata ba shi da alaka da Peter Obi ko ma jaharsa ta Anambra.
Mun ce za mu kai Bill din majalisun dokokin jahohin Kano, Kaduna, Katsina da Jigawa. Mun fara kaiwa majalisar Kano. Washe gari sai mu ka dunguma mu ka tafi Kaduna. Mun je tare da Kamilu Hassan Hamza , Sunusilawan Fandubu da marigayi Saleeth Omar . Akwai kuma Amoke da ya ke a can Kadunan wanda shi ya tattaro ma na 'yan jarida.
'Yan jarida sun yi aikin su. Tun mu na hanyar dawowa mu ka ga labarin cewa shugaban kasa Jonathan ya kira taron gaggawa na majalisar tsaro kan abinda ya ke faruwa a Imo din kuma majalisar ta dakatar da tsarin a koma ina ne.
Mu na dai kan hanyar a ka kira mu a ka ce kwamishinan Sharia na jahar Kano, Maliki Kuliya Umar, ya na son ganin mu. Washe gari mun je wajensa. Da ya ke lokacin su Kwankwaso ba su jima da barin PDP ba don kafa APC. Kwamishinan Shariar ya ce su yanzu sun zama ma su saurin laifi a wurin gwamnatin taraiya. Mun yi abu ana cewa su ne su ka sa mu.
Bayan nan AIG Tambari Yabo ma ya kira mu. Haka ma ofishin DSS na Kano.
Wannan amana ce ta tarihi. Mu fadi abinda da mu a ka yi shi a yadda ya faru. Kuma kamar yadda na fada, ba don suna na ya fito a screenshot ba da ba zan ce komai ba, kamar yadda ban ce komai ba kan wasu abubuwan da da ni aka yi su amma ina gani ana malkwada su. Bahaushe ya ce in mafadin magana wawa ne, to majiyinta ba wawa ba ne. Don haka abinda ake malkwadawar in dai majiyin ba wawa ba ne zai gane.