04/11/2020
LABARIN WANI SARKI MAI HIKIMA.
A can wajajen kasashen gabas
anyi wani
Sarki da ya
dade akan gadon sarauta yana
mulki,da ya
fuskanci ya
tsufa sai ya yanke shawarar yin
murabus,
to amma inda Gizo ke sakar shi ne
wanda zai gaje
shi,maimakon
kawai ya zabi wani daga cikin
yayansa ko
a
mukarrabansa(yan majalisarsa)
sai ya sa aka tara
dukkan samarin garin a
fadarsa,ya ce
musu, "
shekaru
sun cin mini,lokaci ya yi a gare ni
da zan
koma gefe in nada Magaji,kuma a
cikinku na yanke
shawarar
zaba"matasan nan duk s**a rude
wannan
ya kalli
wannan,wancan ya dubi
wancan,zuciyar su cike da tunani, sarkin
ya ci gaba da
cewa"yanzu
zan
ba ku iri na shuka(seed) kowa ya
je ya
shuka shi,ya ba
shi ruwa ya kula da shi har
tsawon shekara guda,a
kawo min na ga irin abin da za ku
samu,duk wanda
na zabi tasa shi ne sabon sarki a
wannan
masarauta.
Aka raba wa matasa iri daban-
daban kowa ya tafi
gida
cike da burin zama sarki idan
shuka ta yi
kyau.
Cikin matasan nan da aka ba
akwai wani da
ake kira
Bilal,da zuwansa gida sai ya
shaida wa
Mahaifiyarsa dukkan yadda ta
wakana a
fadar Sarki,ta
yi murna
da jin wannan labari,nan take ta
taimaka masa
da
tukunya da kasa mai kyau wadda
za tai
saurin
shuka,s**a
shuka irin nan na sarki. Kowace
rana Bilal yakan ba
shuka ruwa,
sai ya yi
tsaye yana kallo ya ga yadda za ta
fito,haka ya yi
ta yi har
wajen sati uku,amma abin
mamaki ba abin da ya
fito
daga kasa,ya zuba ido har zuwa
na hudu na
biyar
kai
har na zuwa shida amma ko
tsagewa kasar ba ta yi
ba,ballatana shuka ta fito.
Zance ba haka yake ba a cikin
gari,domin
matasa
sai
murna suke shukarsu sai girma
take tana yin
kyau,hakan ba karamin tayar da
hankalinsa ya yi ba,sannan ga shi
duk inda
ya je maganar ke
nan,sai ya
yi shiru kurum,bai sanar da kowa
abin da ke faruwa
ba.
A kwana a tashi har wata shida
s**a
shude,matasa
a
gari na cike da farin ciki,shi ko
Bilal na cikin
damuwa,yana ta zuba ruwa ba
shuka,kullum
zuluminsa ya zai fuskanci sarki da
tukunya
ba komai.
Duk nisan wuri za'aje da tafiya saidai a dade ba'aje ba shekara
kwana,in ji yan magana,ranar da
Sarki ya alkawarta ta
cika,gari ya
zama tamkar ranar Sallah,ko'ina
matasa za
ka gani
dauke da tukunyar bishiya iri
daban-daban
sun yi kyau
ga tsayi,sun wa fadar Sarki
tsinke.Amma
al'amarin Bilal
kuwa a wannan rana ya tashi ne
cikin
fargaba har
sai da Mahaifiyarsa ta kwantar
masa da
hankali ta ce "ka je
da abin da ka samu ya fi kin zuwa
kana da
gaskiya,kuma kokarin ka ke nan"
Da shigarsa,sai fada ta kaure da
dariya da
sowa,ana nuna shi da tukunyarsa
ba komai,ya samu
gefe
daga
baya can kurya ya rakabe tare da
sunkuyar da kai
kasa,gabansa na dakan uku-uku.
Can jima wa sai
Sarki ya shgo fada,kowa
ya duka
ya
kai gaisuwa sannan akai shiru
ana
sauraransa,zuci
yoyi cike da fata da burin dacewa
a samu
sarauta,haka
abin
yake ga jama'ar gari wadanda
s**ai dako
ko Allah
zai sa nasu ya fito cikin nasara.
Sarki ya yi
murmushi gami da tashi yana
tafiya
cikin
kasaita da ganin shuke-shuke iri
daban-
daban,"Yau ce ranar da na
alkawarta muku cewa
daya
daga
cikinku
zai zama sabon Sarki a
masarautar nan
kuma na yaba
da abin da idanuna suke gane
min,a saboda da
haka...katsaham ! sai ya hango
tukunya ba komai a
ciki
ga mutum kuma a gefe na boye wa,nan da
nan ya yi
umarni
da a
zo da ita da mai ita,Bilal ya ji wata
rashin lafiya ta
gaba
daya ta k**a shi,cikinsa sai kululu
yake,ya
ji
kafafuwansa sun kasa daukarsa
"shi ke
nan na kashe irina za a kashe ni"
ya fada a
zuciyarsa.bai
gama
tunanin ba ya ji an yi sama da shi sai
gaban
Sarki, ai
tuni sai fada ta rude da dariya da
kyakyatawa
da sowa,wasu
har da faduwa dan mugunta,
Sarki ya daga
hannu
nan
take kowa ya yi shiru,waje ya yi
tsit, "ya
sunanka?" Sarki ya tambaya.
"Suna na Bilal" ya fada
jikisa na rawa.
Sarki ya dube shi sannan ya dubi
taron
jama'a cikin
murya mai karfin sauti da izza ya
ce
" Ku yi gaisuwa ga sabon Sarkinku
mai
suna Bilal". habawa! ai sai wuri ya
rude da gunguni na
mamaki,idanu s**a zazzago baki
a bude
cike da
tambayoyi,ya mutumin da ya kasa
shuka
iri na tsawon
shekara zai zama Sarkinsu?. Bilal
ya d**o kai a firgice,
shin abin da
kunnuwansa
s**a ji gaske ne ko Almara ko
mafarki?
Sarki ya share su ya ci gaba da
maganarsa
kawai,
"Shekarar da ta wuce na ba ku iri
daban- daban a
shuka
a kawo min yau" ya dan nisa can
ya ci
gaba. "To amma ba ku sani ba
DAFAFFEN IRI
na ba
ku (wanda
bazai shuku ba) da kuka ga ya ki
fitowa sai
kuka canza
da wani daban, Bilal ne kadai MAI
GASKIYA
da
bai canza
ba ya kawo min tukunya ba
komai, dan
haka kowa
ya yi gaisuwa ga sabon Sarki" ku
kwashe
wadannan
ciyayin ku ban wuri" Allah kasa
mucika da imani.