15/08/2022
Wani sarki yana auren mata 4.
Ya kasance yana ƙaunar ta 4 sosai, kuma yana duk abin da zai iya yi wajen faranta mata rai.
Yana son ta 3 amma yana ganin da ta samu wanda yafi shi zata rabu da shi.
Ta 2 kuwa duk lokacin d ya shiga matsala ko kuma yake cikin damuwa toh ita take taimaka masa.
Amma ta farko kuwa ba ya wani kula da ita, tare da cewa ita tafi ƙaunarsa.... ita ta ba shi gudummawa wajen gina masarautarsa.
Sarki ya kwanta ciwon ajali. Sai ya tara matansa:
Ya cewa ta 4 shin in n mutu za ki yadda a binne mu tare? Ta ce, wallahi sam ba zan yarda ba.....ta tashi ta yi tafiyarta abinta...!
Ya cewa ta 3 ke fa? Ta ce, sam! Rayuwa akwai daɗi kana mutuwa wani zan aura..! Ta yi tafiyarta..!
Ya cewa ta 2 ke fa? Ta ce, k yi haƙuri ba zan iya ba, mafi girman abin d zan maka in raka ka maƙabarta in za a binneka...!
Ya kalli ta farko cikin yanayi na jin kunya, ya ce toh Saura ke......! Ta ce, na yadda ni zan bika, duk da ka wulaƙantani, ka mayar d ni bani da amfani, ka fifita wasu a kaina....!
Sarki ya fashe da kuka ya ce, wallahi da za a dawo mini da rayuwata baya da na karramaki kuma na girmamaki, da na ƙaunace ki fiye da komai kuma d na baki lokaci na gaba ɗaya...!
Abin fahimta:
Matar farko: Ita ce gangar jikinka, duk yadda ka kai da gyara shi da ƙaunarsa tabbas da ka mutu komai ya ƙare.
Mata ta 2: Dukiyarka da Kadarorinka, kana mutuwa zasu koma hannun wasu...
Mata ta 3: Ƴan uwanka da danginka da Ƴaƴanka.
Mata ta 4: Aikinka na gari, shi kaɗai zai bika amma kuma shi ne bamu damu da shi ba, tare d cewa shi kaɗai zai bi mu Ƙabari.
*Sukairaj Hafiz Imam*