18/05/2026
GOMAN FARKON NA ZUL-HIJJAH SAƘO (22)
1. Allah Madaukakin Sarki Ya Ce:
“Ina rantsuwa da alfijir, da darare goma.”
(Suratul Fajr)
Ibn Kathir رحمه الله ya ce:
“Dararen goma” ana nufin goman farkon Zul-Hijjah. Haka ma Ibn Abbas, Mujahid da sauran malamai s**a bayyana.
2. Allah Ya Ce:
“Domin su ambaci sunan Allah a cikin kwanaki sanannu.”
Ibn Abbas رضي الله عنهما ya ce:
“Kwanakin sanannu” su ne kwanakin goman Zul-Hijjah.
Imam Nawawi رحمه الله ya ce:
Ana son yawaita zikiri a cikin waɗannan kwanaki fiye da sauran kwanaki, musamman ranar Arafah.
3. Manzon Allah ﷺ Ya Ce:
“Babu wasu kwanaki da aikin alheri a cikinsu ya fi soyuwa ga Allah kamar waɗannan kwanaki goma.”
4. Sahabbai S**a Tambaya:
“Ko jihadi ma bai kai ba Ya Rasulullah?”
Sai Annabi ﷺ ya ce:
“Ko jihadi ma bai kai ba, sai mutumin da ya fita da ransa da dukiyarsa sannan bai dawo da komai ba.”
5. Annabi ﷺ Ya Ce:
“Mafi alherin ranakun duniya su ne kwanakin goma.”
6. Azumin Goman Zul-Hijjah
An ruwaito cewa Annabi ﷺ yana azumin kwanaki tara na Zul-Hijjah, ranar Ashura, da kuma kwanaki uku a kowane wata.
7. Yawaita Kabbara
Ibn Umar da Abu Hurairah رضي الله عنهما suna fita kasuwa a cikin waɗannan kwanaki suna yin kabbarori, mutane kuma suna binsu da kabbarori.
Takbiran Zul-Hijjah:
Allahu Akbar, Allahu Akbar,
La ilaha illallah,
Allahu Akbar, Allahu Akbar,
Wa lillahil hamd.
8. Muhimmancin Bayyana Takbiri
Annabi ﷺ ya ce:
“Mutane ba su taru a wani wuri ba face mala’iku suna kewaye da su saboda zikiri.”
Saboda haka ana son bayyana takbiri da zikiri a gidaje, masallatai da kasuwanni.
9. Kokarin yawaita Ibada
Sa’id bn Jubair رحمه الله idan goman Zul-Hijjah s**a shiga yana ƙoƙarin ibada sosai har sai ya gaji.
10. Manyan Goma Uku
Abu Usman An-Nahdi رحمه الله ya ce:
“Salaf suna girmama wasu kwanaki goma uku:
Goman ƙarshe na Ramadan
Goman farko na Zul-Hijjah
Goman farko na Muharram”
11. Falalar Aikin Alheri
Ibn Rajab رحمه الله ya ce:
Idan mutum bai samu damar zuwa Hajji ba, to yin ibada da