11/05/2023
https://www.facebook.com/100044713081579/posts/773231620843934/
MAI HANKALI KE GANEWA:
Wani daga cikin magabata ya ce:
Ka bar sirrinka a tsakanin abu biyu: RANKA DA UBANGIJINKA.
A duniya ka yi kwaɗayin samun yardan abu biyu: MAHAIFIYA DA MAHAIFINKA.
A ya yin tsanani ka nemi taimakon Allah da abubuwa biyu: HAƘURI DA SALLAH.
Kar ka ji tsoron abubuwa biyu: ARZIKI DA MUTUWA domin suna hannun Mai Rahama ne.
Abubuwa biyu kar ka ambace su: KYAUTATA DA KA YI MA MUTANE DA MUNANAWAN DA MUTANE S**A YI MAKA.
Abubuwa biyu kar ka manta da su har abada: ALLAH DA GIDAN LAHIRA.
✍️ UMAR SHEHU ZARIA
18 Shawwal, 1444
(08/05/2023)