26/07/2026
A lokacin da Nasir Ahmad El-Rufai yake Gwamnan Jihar Kaduna, blogger irin Nagya a Kaduna. Kowace rana yana yana s**ar El-Rufai tun daga safe har zuwa dare, har ma yana kiransa da ɓarawon kuɗin gwamnati.
Sai dai El-Rufai bai sa aka k**a shi ba. Maimakon haka, ya nemo lambar wayarsa.
Wata rana El-Rufai ya kira shi da kansa.
Wayar ta shiga...
El-Rufai: Assalamu alaikum, barka da safiya.
Blogger: Barka da safiya. Don Allah da wa nake magana?
El-Rufai: Sunana Nasir Ahmad El-Rufai.
Blogger: Oh, barka da safiya, Mai Girma.
El-Rufai: Barka da safiya, ɗan'uwa. Ina ganin rubuce-rubucenka game da gwamnatina da kuma yadda kake zargina da wawure kuɗin jiha.
Blogger: Yi haƙuri ranka ya daɗe, ba haka nake nufi ba.
El-Rufai: Ba damuwa. Hakan yana cikin shugabanci. Amma zan so ka zo Gidan Gwamnati gobe domin mu tattauna waɗannan batutuwa. Kada ka ji tsoro, babu abunda zanma.
Blogger: Ba matsala, ranka ya daɗe. Wane lokaci zan zo?
El-Rufai: Karfe 10:00 na safe.
Blogger: In shaa Allah zan zo.
El-Rufai: Zan jira ka. Amma za ka zo da mota ne ko babur? Domin na sanar da jami'an tsaro su bar ka ka wuce.
Blogger: Zan hau adaidaita sahu ne.
El-Rufai: To idan kana kan hanya ka turo min da lambar adaidaita sahun, domin in sanar da jami'an tsaro.
Blogger: To, babu matsala.
Washegari da misalin ƙarfe 9:00 na safe, blogger ɗin ya hau adaidaita sahu ya nufi Gidan Gwamnati. Da ya isa ƙofar shiga, jami'an tsaro s**a bari ya wuce, har s**a nuna masa inda zai tsaya.
Daga nan sai ADC na gwamnan ya zo ya raka shi kai tsaye zuwa ofishin gwamnan.
Da ya shiga ofishin, El-Rufai ya tambaye shi:
El-Rufai: Ka biya kuɗin adaidaita sahun?
Blogger: A'a, ranka ya daɗe.
Sai El-Rufai ya buɗe drawer shi, ya fito da wata ambulan mai ɗauke da ₦250,000, ya ba shi ya je ya biya kuɗin adaidaita sahun sannan ya dawo.
Blogger ɗin ya karɓa. A hanya sai ya buɗe ambulan, ya cire ₦5,000, ya ɓoye sauran kuɗin. Da ya isa wajen direban adaidaita sahun, sai ya ba shi ₦5,000. Direban ya yi farin ciki sosai.