20/12/2025
Mai bai wa gwamnan shawara kan harkokin tsangayu, Gwani Musa Hamza Falaki ne ya miƙa cekin kuɗin ga gwarzuwa, Hafsat Muhammad Sada, yayin rufe musabaƙar a Maiduguri.
Gwani musa ya taya gwamna Abba Kabir Yusuf da al’ummar Kano murna bisa samun nasara ta gwarzuwar shekarar ta musabakar Al-ƙur'ani ta ƙasa, wadda ƴar asalin jihar Kano ce.
Da kuma sauran ɗaliban Kano da s**a samu nasara a matakai daban-daban na musabaƙar.