11/05/2026
Haske Ya Girgiza Adamawa Yayin Da Yake Cigaba Da Zagaye A Fadin Jahar
Dan siyasar nan mai tasowa kuma jigo a jam’iyyar APC, Haske, ya kara daukar hankalin al’ummar Jahar Adamawa bayan fara rangadin ganawa da jama’a a fadin kananan hukumomin jihar.
A yau Litinin ne aka fara wannan zagaye inda aka tsara ziyartar kananan hukumomin Toungo, Ganye, Jada da Mayo-Belwa domin tattaunawa da jama’a tare da jin koken su da kuma bayyana manufofin cigaban da ake da su ga jihar.
Tun bayan bayyana jadawalin wannan “Engagement Tour” ne mutane da dama s**a fara bayyana ra’ayoyinsu a kafafen sada zumunta, inda wasu ke ganin wannan yunkuri alama ce ta kusanci da jama’a da kuma kokarin hada kan al’ummar Adamawa.
Masu bibiyar harkokin siyasa a jihar sun bayyana cewa yadda jama’a ke nuna goyon baya ga Haske na kara fito da irin farin jinin da yake samu musamman tsakanin matasa da masu ruwa da tsaki a siyasance.
Jadawalin ya nuna cewa bayan kammala zagayen ranar Litinin, za a ci gaba da kai ziyara zuwa wasu kananan hukumomi daban-daban daga ranar Talata har zuwa Juma’a, domin tabbatar da cewa an kai ga al’umma a kowane yanki na jihar.
Wasu daga cikin magoya bayan sa sun bayyana wannan zagaye a matsayin wata dama ta kara dankon zumunci tsakanin shugabanni da talakawa, tare da nuna cewa irin wannan mataki yana kara karfafa siyasar APC a Adamawa.