22/06/2026
TO IDAN AURE BA SHI DA AMFANI, ME YASA ALLAH DA MANZONSA S**A KWADAITAR DA SHI?
Wata fitacciyar yar fim,
Nafisa Abdullahi,
ta fito tana bayyana ra'ayinta game da aure.
Ta ce:
Mutane suna cewa amfanin aure shi ne ka haifi 'ya'ya
domin idan ka mutu su maka addu'a.
Amma ni ina da iyali da suke sona,
Kuma idan na mutu za su ci gaba da yi min addu'a.
Sannan wa ya tabbatar maka cewa yaran
da ka haifa za su maka addu'a bayan mutuwarka?
Ba ka da wannan tabbacin.
Don haka wannan ba hujja ba ce ta yin aure.
Idan mutum yana son aure ya yi ne saboda yana so,
Ba wai saboda za a masa addu'a ba.
Wannan magana ta sa mutane
da yawa s**a fara muhawara.
Wasu sun yarda, wasu kuma sun nuna
Cewa aure a Musulunci ya fi wannan fahimtar nesa.
Allah Ya jikan Sheikh Muhammad Auwal Albani Zariya
Rahimahullah, ya taba yin bayani mai zurfi
A kan darajar aure. Ya ce:
Jama'a, babu abin da ya kai aure lada.
Sannan ya kawo hadisi cewa
Manzon Allah ﷺ ya bayyana irin girman ladan
Da mace take samu a rayuwar aurenta.
Malam ya ce:
Mace idan ta tashi daga dakin mijinta
Zuwa kitchen ta dawo,
Allah yana rubuta mata ladan Umrah.
Ya ce ko ta manta albasa ta koma ta dauko ta dawo,
Ladan Umrah. Ta manta wuka ta sake komawa ta dawo,
ladan Umrah.
Malam yana son ya nuna cewa rayuwar aure
ba kawai zama tare ba ce.
Akwai tarbiyya, ibada, hidima, hakuri, soyayya
da kuma lada masu yawa da Allah Ya boye a cikinta.
Sannan Malam ya kara da cewa:
Karatu ana yi ne domin neman ilimi,
ba domin tara kudi kawai ba.
Ma'ana, Musulunci bai hana neman ilimi ko aiki ba,
amma bai kamata mutum ya manta da darajar
Abubuwan da Allah da Manzonsa s**a kwadaitar da su ba.
Hakika, gaskiya ne babu wanda zai iya tabbatar
maka cewa danka zai maka addu'a bayan mutuwa.
Amma kuma babu wanda zai iya tabbatar
Maka cewa ba zai maka ba.
Shi ya sa Manzon Allah ﷺ ya ce idan mutum ya mutu,
ayyukansa suna yankewa sai wasu abubuwa,
Daga cikinsu akwai:
Da na nagari wanda yake masa addu'a.
Don haka samun ɗa nagari da zai ci gaba da yi maka addu'a
wata babbar ni'ima ce, ko da yake ba ita kaɗai ce
manufar aure ba.
Aure a Musulunci ba kawai haihuwa ba ne.
Ibada ne, kariya ce daga fitina, gina al'umma ce,
Samun zuri'a ta gari ce, samun nutsuwa ce,
sannan hanya ce ta neman yardar Allah.
Allah Ya sa mu fahimci addininmu yadda ya kamata,
Ya ba samari da 'yan mata mazaje da mata nagari,
Ya sanya albarka a cikin auren Musulmai,
Ya kare mu daga fahimtar da za ta sa mu raina
abin da Allah da Manzonsa s**a daukaka. Ameen.
🤲 Allah Ya jikan Malam Muhammad Auwal Albani Zariya Rahimahullah. Duk wanda ya amfana da iliminsa ko ya saurari wa'azinsa,
Allah Ya sa wannan ilimin ya ci gaba da gudana
A mizanin ayyukansa har zuwa ranar Alƙiyama.
Ameen.
🤲 Masu sharing wannan saƙo, Allah Ya saka muku da alkhairi,
Ya buɗe muku ƙofofin rahama da arziki,
Ya azurta ku da zuri'a ta gari,
Ya sa mu dace da Sunnah a rayuwarmu da bayan mutuwarmu.
Ameen.
Coppied from ✍️Addinu Annasiha